

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Rundunar yan sandan Jihar Jigawa ta kama wasu yan Bindiga 5 wanda suke addabar Jihohin Jigawa da Kano ta fuskar yin garkuwa da mutane a yankunan.
Kakakin rundunar yan sandan Jihar Jigawa ASP Lawan Shiisu Adam, shine ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse.
A cewarsa, yan sanda sun samu bayanan sirri kan wani Kasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna Yusuf Wakili wanda akafi sani da Rago inda suka samu nasarar kamashi a karamar hukumar Ajingi ta Jihar Kano.
Haka kuma ya ce sun kama kasurgumin mai garkuwa da mutanen ne tare da Inusa Jibrin, Alh Tahir Zango, Sabo Abdullahi Alias Sabo Gara da Suleman Garba wand aka fi sani da Manu Dogo.
ASP Lawan Shiisu Adam, ya ce Mutanen sun amince da aikata laifukan sace-sacen mutane a Jihohin Kano da Jigawa.
Yan sanda sun kwato bindiga 1 tare da wasu harsashe daga hannun yan bindigar.
Kakakin rundunar yan sandan ya ce an tura mutane zuwa sashen bincikar manyan laifuka.