

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya ce mutuwar matasa 29 a wani hatsarin kwale-kwale a kauyen Gidan-Magana da ke karamar Hukumar Shagari a Jihar Sakkwato, abin takaici ne.
Alhaji Sa’ad Abubakar ya bayyana ra’ayinsa ne a jiya a ziyarar jaje ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, da jama’a da gwamnatin jihar Sokoto a kan iftila’in da ya afku a ranar Laraba.
Sarkin Musulmin, wanda ya samu wakilcin Sarkin Kabin Yabo, Alhaji Muhammadu Maiturare, ya bayyana lamarin a matsayin kaddara daga Allah madaukakin sarki.
Yanzu haka Sarkin Musulmin yana kasar Saudiyya yana gudanar da Umrah.
Idan dai za a iya tunawa, matasan sun rasa rayukansu ne a ranar Laraba a lokacin da kwale-kwalen da suke tafiya a cikin kogin Shagari domin neman itace ya kife.
Daga cikin wadanda suka mutu, 23 mata ne, 6 maza, yayin da aka ceto mutane shida da ransu.