Sarkin Musulmi yayi alkawarin hukunta wayanda suka kashe Deborah wacce ake zargi da batanci ga Manzon Allah

0 126

Mutane dayawa sun tofa albarkacin bakinsu a jiya bayan kisan da aka yi wa Deborah Samuel, wata dalibar Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sakkwato, bisa zarginta da yin batanci.

An rawaito cewa dalibar dake matakin karatu na biyu ta yi kalaman batanci ga fiyayyen halitta a group din WhatsApp.

Gwamnatin jihar Sokoto ta mayar da martani inda ta bayar da umarnin rufe kwalejin cikin gaggawa.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar ta ce an kama wasu mutane biyu da ake zargi da hannu a kisan dalibar yayin da aka fara farautar sauran wadanda ake zargi da suka tsere.

A halin da ake ciki, Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya yi Allah wadai da kisan da aka yi wa dalibar.

Sarkin, a wata sanarwa da sakataren Majalisar Sarkin Musulmi ya fitar, ya bukaci da a kamo tare da hukunta dukkan wadanda suka aikata kisan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: