Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne – Kwankwaso

0 56

Tsohon gwamnan jihar Kano, sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya soki ƴan siyasar da ke sauya sheƙa bayan sun gama cin moriyar jam’iyyar, abin da ya bayyana da babban kuskure a siyasance.

Sanata Kwankwaso wanda ya bayyana hakan a Kano lokacin da yake karɓar wasu ƴan siyasar da suka sauya sheƙa zuwa NNPP daga ƙaramar hukumar Takai, a gidansa da ke Miller road a birnin Kano.

A baya-bayan nan ne dai raɗe-raɗi suka yi ta yawo cewa Kwankwason zai koma jam’iyya mai mulki ta APC.

Rabi’u Kwankwaso ya ƙara jaddada irin juriya da haɗin kai da ke tafiyar Kwankwasiyya duk kuwa da cewa an ta ƙoƙarin ganin an kawar da hankalin mabiya.

Leave a Reply