

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a jiya ya kaddamar da kwalbati mai tsayin kilomita 7.6 domin magance zaizayar kasa a karamar hukumar Jama’are ta jihar Bauchi.
Shugaban kasar, wanda ya samu wakilcin karamar ministar masana’antu, kasuwanci da zuba jari, Maryam Yalwaji Katagum, yace an gudanar da aikin ne domin dakile wahalhalun da mazauna wajen ke fuskantar.
Shugaba Buhari aiki zai magance babbar matsalar yanayi dake fuskantar mazauna wajen.
Yace gwamnatin tarayya ta gudanar da manyan ayyukan dakile zaizayar kasa a garuruwa da kauyuka dayawa a fadin kasarnan.
Da yake yabawa dan kwangilar saboda ingancin aikin, shugaban kasar ya bukaci mazauna wajen da su tabbatar da sun yi amfani da aikin ta hanyar da ta dace tare da tsare shi daga bata gari.
A nasa jawabin, gwamnan jihar, Bala Abdulkadir Mohammed, ya yabawa shugaban kasa bisa aikin.