

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana bakin cikinsa kan kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa gomman ‘yan sa kai a Jihar Kebbi.
Sawaba ta ruwaito yadda ‘yan bindigar suka yi wa ‘yan sa-kai kwanton bauna a karamar hukumar Sakaba ta jihar Kebbi, inda suka kashe akalla 63 daga cikinsu.
‘Yan sa kan sun fito ne daga kauyuka biyar na Takita, Magajiya, Rafin Zuru, Dabai da Sanci.
Shugaban kasar ya bayyana ra’ayinsa ne a wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar jiya a Abuja.
Ya kuma bayyana wannan mummunar aika aika a matsayin abin ban mamaki, sannan ya yi kira ga jami’an tsaro da su kara kaimi tare da rubanya kokarinsu domin dakile shirin ayyukan ‘yan ta’addan kafin ma su kai hare-hare.
Shugaban kasar ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta yi duk abin da ya kamata don magance ‘yan fashi da tsautsayi.