

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Wani ɗan jarida a Jamhuriyyar Dimokraɗiyyar Kongo ya rasu sakamakon raunin da ya samu sakamakon harbinsa da bindiga da aka yi a lokacin da ƴan sanda suka yi arangama da yan bindiga a ƙasar.
Jean-Marie Luzingu na a Kinshasa a lokacin da aka samu arangamar.
Wani harsashi da wani ɗan sanda ya harba ne ya samu ɗan jaridar, kamar yadda wani wanda ya shaida lamarin ya bayyana wa Mishapi Voice Radio.
Ƴan uwansa yan jarida dai na ci gaba da jimamin mutuwarsa a shafin Twitter.
A halin yanzu ana ci gaba da bibiya domin gano waɗanda suka haddasa wannan tarzomar.
Ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasar ta ce tana buƙatar a bi wa wanda aka kashe haƙƙinsa.
Asalin labarin: BBCHausa;
https://www.bbc.com/hausa/live/labarai-59695622