Wani jirgin ruwa ya kife inda mutum 28 suka mutu a ciki yayin hatsarin a Sakkwato

0 74

Hukumomi a jihar Sakkwato da ke Najeriya sun tabbatar da mutuwar mutane 28 a cikin wani hadarin jirgin ruwa da ya faru a yankin karamar hukumar Shagari.

Lamarin dai ya faru ne da yammacin jiya Talata yayin da matafiyan ke kokarin tsallaka Kogi daura da garin Gidan-Maa-gana.

Shugaban Karamar Hukumar Shagari Alhaji Aliyu Dantani Shagari ya galibin wadanda suka rasun mata ne da kananan yara

Sai dai kawo yanzu ba a iya tantance ko mutane nawa ke cikin jirgin ba lokacin da ya kife don haka masu ninkaya ke can suna lalabe don tsamo karin gawwaki ko kuma samun wanda ya tsira daga hadarin.

Hadarin jirgin ruwa dai ba bakon abu ba ne a wannan yankin kuma galibi akan ta’allaka faruwarsa ga daukar mutane da kaya fiye da kima da rashin amfani da riguna kariya daga nutsewa da rashin kyawon yanayi da sauransu

Ko a watan Yunin bara ma mutane a kalla 13 ne suka rasa rayukansu a yankin na Shagari sakamakon kifewar da jirgin da suke tafiya a ciki ya yi lokacin da suke kan hanyarsu ta dawowa daga wani bukin aure.

BBCHausa

Leave a Reply

%d bloggers like this: