Wasu rahotanni da suke fitowa daga Kasar Sudan na cewa an yi juyin mulki a kasar

0 65

Wasu rahotanni da suke fitowa daga Kasar Sudan na cewa an yi juyin mulki a kasar.

sannan an kama mambobin gwamnatin rikon kwarya a kasar.

Fira ministan kasar Abdallah Hamdok, da wasu ministoci hudu na daga cikin wadanda aka yi amanna cewa wasu sojoji da ba a tantance ko su waye ba sun kama tare da tsare su a safiyar yau Litinin.

Sojoji dai basu ce komai ba kawo yanzu game da juyin mulkin.

Wata sanarwa daga ma’aikatar yada labaran kasar ta wallafa a shafinta na Facebook cewa wata hadakar rundunar sojojin kasarce ta kama fira ministan da ministocin hudu in da ake tsare da su a wajen da ba a bayyana ba.

Rahotanni sun ce an katse layukan sadarwa a kasar.

Sannan, an bada rahoton cafke mai bai wa mista Hamdok shawara kan harkokin yada labarai.

Tuni Kungiyar kwararru a Sudan sun yi kira ga jama’a da su fito kan tituna domin nuna bijirewa juyin mulki.

Leave a Reply

%d bloggers like this: