- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Wata babbar kotun jiha dake zamanta a Birnin Kudu ta zartar da hukuncin daurin rai da rai ga wani mai suna Isa Ibrahim Kwari dake kauyen Kwari na karamar hukumar Birnin Kudu bisa laifin aikata fyade.
Da yake zartar da hukuncin, Alkalin kotun Mai shari’a Musa Ubale ya bayyana cewa kotun ta samu wadda ake kara da laifin yiwa yarinya ‘yar shekara hudu fyade a gonar sa a wani lokaci cikin shekara ta 2018.
Kotun ta gamsu da shedun da lauya mai gabatar da kara ya gabatar mata, inda ta tabbar da wanda ake kara da aikata laifin, don haka kotun ta zartar masa da hukuncin daurin rai da rai karkashin sashi na uku na kundin laifuka na Penal Code na jihar Jigawa wanda aka yiwa gyara a shekara ta 2014.
Daraktan sashin ayyuka na musamman da harkokin baki na hukumar shari’a ta jihar Jigawa, Abbas Rufa’i Wangara, ya ce kotun ta zartar da hukuncin ne a zaman data yi a garin Birnin Kudu.