Wata gagarumar girgizar kasa da ta faru a Afghanistan ta yi sanadin mutuwar akalla mutum 920

0 72

Wata gagarumar girgizar kasa da ta faru a Afghanistan ta yi sanadin mutuwar akalla mutum 920 sannan da dama sun jikkata, a cewar shugaban addinin kasar.
Hotuna sun nuna yadda kasa take zaftarewa sanna ta lalata gidajen-kasa a lardin Paktika da ke gabashin kasar, inda masu aikin ceto suke can suna yi wa wadanda suka jikkata magani.
A wuraren da ke da wahalar zuwa, an aike da jiragen helikwafta domin dauko wadanda suka jikkata don a kai su asibit.
Shugaban Taliban Hibatullah Akhundzada ya ce daruruwan mutane sun lalace kuma mai yiwuwa mutanen da suka mutu za su karu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: