- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Wata Babbar Kotun Jihar Jigawa wanda take zamanta a Birnin Kudu a jiya Juma’a ta yankewa Isa Ibrahim, hukuncin daurin rai-da-rai bisa samun sa da laifin yiwa wasu Yara Kanana Yan Gida Daya Fyade a kyauyen Kwari dake Karamar Hukumar Birnin Kudu.
Mai Gabatar da kara Shu’aibu Aminu, ya fadawa Kotu cewa a ranar 26 ga watan Satumba ne aka gabatar da Mutumin a gaban Kotu kan zargin yin lalata da Yaran Yan shekara 4 da 5 a Gonar sa.
Lauya mai gabatar da Kara ya gabatarwa da Kotu shaidu 5 wanda suke tabbatar da cewa mutumin ya aikata laifukan da ake zargin sa da su.
Da yake yanke hukuncin, Alkalin Kotun Mai Shari’a Musa Ubale, ya ce fyaden ya ci karo da sashe na 282 (1) na Manyan Laifuka wato Penal Code.
Kazalika, Mai Sharia Musa Ubale, ya yankewa Isah Ibrahim hukuncin bayan samun sa da laifukan da ake zargin sa da su.