Yadda akai yan bindiga su kai hari kan jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja

0 104

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari kan jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja, lamarin da ya tilasta wa jirgin ya tsaya a tsakiyar hanya.

An raiwaito cewa yan bindigan sun fara kai farmaki kan jirgin a jiya da daddare kuma sun samu nasarar tsayar da shi.

‘Yan bindigar, a cewar majiya, sun sake dawowa da safiyar yau, inda suka dasa nakiyoyi akan hanyar jirgin kasa.

Wani ma’aikacin Hukumar Jiragen Kasa da ya nemi a sakaye sunansa, ya sanar da cewa sun fuskanci harbe-harbe, kuma jirgin ya tsaya yayin da harbe-harben suka lalata tankin mai.

Hukumar Jiragen Kasa kazalika ta tabbatar da cewa nakiyoyin da aka dasa sun tashi akan hanyar jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja, amma ba a san wadanda suka dasa ba.

Manajan daraktan hukumar, Fidet Okhiria, wanda ya zanta da manema labarai ya bayyana cewa abubuwan fashewar sun lalata digar jirgin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: