

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Mahaifiyar wani dan majalisar dokokin jihar Kano, Isyaku Ali, da aka sace, ta shaki iskar ‘yanci bayan biyan kudin fansa na naira miliyan 40.
‘Yan bindiga sun sace Hajiya Zainab a ranar 12 ga watan Janairu a gidanta dake karamar hukumar Gezawa ta jihar Kano.
Dan ta, Isyaku Ali, tsohon kakakin majalisar dokokin ne kuma a yanzu shine shugaban masu rinjaye a majalisar.
A yau da safe, dan majalisar ya tabbatar ta sakin mahaifiyar ta sa ga manema labarai a Kano. Yace shi da wasu mutane suna kan hanyarsu ta zuwa dauko ta a jihar Jigawa inda barayin suka sake ta.
A wani labarin kuma, jam’iyyar PDP reshen jihar Kano, ta yi kira ga gwamnatin jihar Kano, karkashin shugabanci Abdullahi Umar Ganduje, da kada ta yi amfani da kisan Hanifah a matsayin hanyar tatsar kudade daga masu makarantun kudi.
Biyo bayan kisan Hanifah Abubakar yar shekara 5 a hannun Abdulmalik Abubakar, mamallakin makarantar Noble Kids dake yankin karamar hukumar Nasarawa ta jihar, gwamnatin jihar ta soke dukkan lasisin makarantun kudi a jihar.