‘Yansanda sun fara bincike akan mutuwar Abdulkarim Na Allah

0 107

‘Yansanda sun fara bincike akan mutuwar Abdulkarim Na Allah, duk da kasancewar gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana lamarin da mai kama da kisan kai.

Mamacin da ne a wajen Sanata Bala Na’Allah.

Kwamishinan yansanda na jihar Kaduna, Mudasiru Abdullahi, ya bayar da umarnin bincike akan lamarin.

Kwamishinan ya bayar da umarnin a daren jiya a Kaduna, cikin wata sanarwa da kakakin yansandan jihar, Mohammed Jalige, ya fitar.

An rawaito cewa an kashe matukin jirgin sama mai shekara 36 jiya a gidansa dake Kaduna.

‘Yansanda sun nemi jama’ar gari da su taimaka da bayanai masu muhimmmanci dangane da binciken kisan kan.

A nasa bangaren, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya bayyana matsayar gwamnatin jihar cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a Abuja.

Leave a Reply

%d bloggers like this: