Yau ake gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnoni a APC

0 79

A yau ne wanda yake 26 ga watan Mayun 2022 za a gudanar da zaɓen fitar da gwani na ƴan takarar gwamnonin jam’iyyar APC mai ci. Hakazalika, ana kyautata zaton a yau ɗin ne za a gudanar da zaben fitar da gwani na ƴan majalisar wakilan tarayya.


Anan jihar Jigawa yan takara mutum tara (9) ne za su fafata a zabukan fitar da gwanin na takarar gwamna.


A wani kaulun, ana kyautata zaton a wasu jihohin za a samu maslaha ko kuma abinda ake cewa sasanci domin fitar da ɗan takara guda ɗaya wanda zai jagoranci zabe a 2023.

Leave a Reply

%d bloggers like this: