A yau ne wanda yake 26 ga watan Mayun 2022 za a gudanar da zaɓen fitar da gwani na ƴan takarar gwamnonin jam’iyyar APC mai ci. Hakazalika, ana kyautata zaton a yau ɗin ne za a gudanar da zaben fitar da gwani na ƴan majalisar wakilan tarayya.
Anan jihar Jigawa yan takara mutum tara (9) ne za su fafata a zabukan fitar da gwanin na takarar gwamna.
A wani kaulun, ana kyautata zaton a wasu jihohin za a samu maslaha ko kuma abinda ake cewa sasanci domin fitar da ɗan takara guda ɗaya wanda zai jagoranci zabe a 2023.