

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Gwamnatin jihar Jigawa ta jaddada kudirinta na cigaba da kare rayuka da kuma dukiyoyin alummar jiharta.
Daraktan tsaftar mahalli na Hukumar Kare Mahalli ta jiha Alhaji Nuhu Yusif shine ya bada wannan tabbaci a lokacin da yake duba aikin tsaftar mahalli da hukumar take gudanarwa a garin Gumel.
Yace sakamakon mamakon ruwan sama da ake tafkawa a sassan jihar nan ya zama wajibi hukumar ta gudanar da aikin yashe magudanan ruwa da kwalbatoci domin gudun ambaliyar ruwa da wasu yankuna suke fuskan ta.
Alhaji Nuhu Yusif ya kara da cewar za su gudanar da aikin yashe kwalbatoci da magudanan ruwan ne na kwanaki 12 a shiyyoyin Gumel da Ringim.
Daga nan sai ya bukaci al’umma da su guji zuba shara a magudanan ruwa domin gudun ambaliyar ruwa.