

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na sake tattaunawa kan yanayin aikin dukkan ma’aikata a jami’o’in gwamnati dake fadin kasar nan.
Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Chris Ngige ne ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kwamitin sulhu na gwamnatin tarayya da na jami’o’i na shekarar 2009 karkashin jagorancin shugaban kwamitin, Nimi Briggs, jiya a Abuja.
Chris Ngige ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai rike da mukamin shugabar ‘yan jaridu da hulda da jama’a a ma’aikatar, Patience Onuobia.
Ministan yana magana ne kan yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta ke gudanarwa.
Ya ce a matsayinsa na mai shiga tsakani, ya dade yana ta kokarin ganin an aiwatar da duk wani abu da ke kunshe a cikin yarjejeniyar fahimtar juna ta shekarar 2020 wacce gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU suka sanya wa hannu.