Rundunar ‘yan sandan Jihar Abia ta cafke wani matashi mai suna Ebere Christian Sunday bisa zargin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 13 a yankin Obehie da ke ƙaramar hukumar Ukwa West a jihar.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Danladi Isa, ya bayyana cewa an kama wanda ake zargin ne mai shekaru 27 a ofishin ‘yan sanda na Obehie, bayan samun bayanai kan aikata laifin.
A cewarsa, wanda ake zargin ya aikata laifin ne tare da wasu abokansa biyu maza, waɗanda har yanzu ba a kama su ba sun tsere, inda ya ƙara da cewa sun yi wa yarinyar barazana da makami idan ta yi ihu ko ta sanar da mahaifiyarta abin da ya faru.
“Wanda ake zargin ya amsa laifinsa, kuma muna ci gaba da ƙoƙarin kamo sauran waɗanda suka tsere,” in ji kwamishinan.
Ya kuma bayyana cewa an kwato wasu kayayyakin shaida daga hannun wanda ake zargin, ciki har da wuka, tufafi da suka yage, da kuma wasu kaya masu ɗauke da jini.
An gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu domin fuskantar hukunci bisa laifin da ake zarginsa da aikatawa.
A wani lamari makamancin haka, rundunar ta kuma kama wasu mutane biyu — Chizuruoke Monday da Onyekachi Onyema — bisa zargin satar jaririya ‘yar makonni biyu.
Rahotanni sun nuna cewa ana zargin mutanen biyu da satar jaririyar ne daga wajen wata mata mai fama da matsalar kwakwalwa a watan Afrilu na shekarar 2020, kafin su tsere daga yankin.
Kwamishinan ya ce bincike na ci gaba a sashen binciken manyan laifuka (SCID) da ke Umuahia, inda ake ƙoƙarin gano waɗanda suka sayi jaririyar tare da ceto ta.
Bugu da ƙari, rundunar ta ce ta samu nasarori a yaƙi da ayyukan kungiyoyin asiri, inda aka binciki shari’o’i 13, aka kama mutane 23 tare da gurfanar da su a kotu, sannan aka kwato makamai 32.
Haka kuma, rundunar ta miƙa tallafin kuɗi da ya kai naira miliyan 11.9 ga iyalan jami’an ‘yan sanda da suka rasu, a wani ɓangare na ƙoƙarinta na tallafa wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu yayin aiki.