Atiku da Obi suna shirin hade kai a kan zaben 2027

Wani aminin tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa Atiku na da niyyar hada kai da Peter Obi, domin su kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.

Majiyar ta bayyana cewa dukkanin jagororin za su iya jawo Tinubu ya rasa kujerarsa matukar suka yi aiki tare a kakar zabe mai zuwa.

A cewar majiyar, wadda ta bayyana hakan a wata hira da jaridar The Punch, Atiku da Obi sun gane cewa ba za su iya cimma burin shugabanci nagari a Najeriya ba sai sun hada kai.

Majiyar ta kara da cewa wannan dalili ne ya sa suka yanke shawarar fara aiki tare, duk da cewa har yanzu ana tattaunawa cikin sirri.

Comments (0)
Add Comment