Dole Ne Iran Ta Kashe Kuɗin da Za Mu Sakar Mata A Cikin Amurka – Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake nanata cewa duk wani kuɗin Iran da aka riƙe, wanda za a saki sanadiyyar ɗage takunkumai da gwamnatin Amurka ta yi, za a tura kuɗin ne zuwa cikin wani asusu na musamman wanda ke ƙarƙashin kulawar Amurkar.

A wani saƙo da ya wallafa a shafin sada zumunta, Mista Trump ya ce daga cikin asusun ne Iran za ta iya amfani da kuɗin wajen sayen abinci da magunguna, kuma daga Amurka kawai za ta saya.

A baya Iran ta yi watsi da sharuɗɗa makamantan haka daga mataimakin shugaban Amurka J.D Vance wanda ya jagoranci tattaunawar sasanci da Iran a ƙasar Switzerland.

Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya a birnin Geneva ya ce Iran ce kadai take da ƴancin tantance yadda za ta yi, da kuma abin da za ta yi da kadarorinta da za a saki.

Comments (0)
Add Comment