Gwamnan jihar Yobe ya yi kira da a gudanar da bincike don gano musabbabin jefo bama-bam a kauyen Buhari

Gwamna Mai Mala Buni na jihar Yobe ya yi kira da a gudanar da bincike don gano musabbabin jefo bama-bama daga jirgin sama da yayi sanadiyar rayuka a kauyen Buhari, karamar hukumar Yunusari a jihar Yobe.

An bayar da rahoton cewa akalla mutane 8 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka samu raunuka lokacin da wani jirgin sama ya jefo bama-bamai kan mutanen kauyen a jiya da safe.

Mai magana da yawun rundunar sojin sama, Air Commodore Edward Gabkwet, ya nisanta rundunar daga faruwar lamarin.

A cikin wata sanarwa da Babban Daraktan yada labarai, Mamman Mohammed, Gwamnan ya yi ta’aziyya da iyalan wadanda suka rasa rayukansu a lamarin.

Mai Mala Buni ya kuma bayar da tabbacin shirye-shiryen gwamnatinsa don yin aiki tare da dukkan jami’an tsaro don tabbatar da tsaron jihar.

A halin da ake ciki, gwamnan ya umarci asibitocin gwamnati da ke garuruwan Geidam da Damaturu da su bayar da magani kyauta ga wadanda suka samu raunuka sakamakon harin.

Comments (0)
Add Comment