Gwamnan jihar Zamfara ya yi alkawarin tsai da kudurin magance ma’aikatan da ke karbar albashi da yawa a jihar

Gwamna Dauda Lawal na Zamfara, ya yi alkawarin tsai da kudurin magance ma’aikatan da ke karbar albashi da yawa a ma’aikatan gwamnati.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake jawabi a wajen bikin ranar ma’aikata na 2024 da aka gudanar a Gusau.

Ya kuma shawarce su da su marawa gwamnati mai ci baya a kan kudirin ta na tsaftace ma’aikatan jihar, sannan ya bukace su da su guji duk wani nau’i na cin hanci da rashawa duba da yadda ma’aikatan jihar ke cika makil da masu karbar albashi.

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa na kan aikin tantance ma’aikatan jihar da kananan hukumomi na hakika, inda ya tabbatar da cewa da zarar an gama da ma’aikatan bogi, masu yawan albashi da sauran kura-kurai, za a sanar da sabon mafi karancin albashi.

A nasa jawabin, shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya NLC reshen Zamfara, Sani Haliru ya yabawa kokarin gwamna Lawal na magance matsalolin tsaro da ke addabar jihar.

Comments (0)
Add Comment