Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, na shan suka bayan wani bidiyo da ya bazu a kafafen sada zumunta inda ya bayyana aniyarsa ta tabbatar da nasarar jam’iyyar APC a zaben kansilolin Babban Birnin Tarayya, duk da matsalolin tsaro da ke addabar sassan jiharsa.
A cikin bidiyon da aka dauka yayin wani taron siyasa, gwamnan ya ce zai hada kai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa jam’iyyar APC ta samu nasara a dukkanin kananan hukumomi shida na Abuja. Ya jaddada cewa jam’iyyar ita ce ginshikin ci gaba mai dorewa a Najeriya.
Sai dai kalaman nasa sun jawo ce-ce-ku-ce, inda mutane da dama suka yi tambaya kan dalilin mayar da hankali kan siyasar Abuja alhali wasu al’ummomi a Kwara na fama da hare-haren ‘yan bindiga da garkuwa da mutane.
Wannan ce-ce-ku-ce na zuwa ne bayan wani bidiyo mai tayar da hankali ya bayyana, wanda ake zargin ‘yan ta’adda ne suka fitar, yana nuna wasu daga cikin mutanen da aka sace a harin da aka kai kauyen Woro da ke karamar hukumar Kaiama a ranar 3 ga Fabrairu.
Gwamnatin Jihar Kwara, ta bakin Kwamishinar Sadarwa, ta ce tana aiki tare da jami’an tsaro domin nazarin bidiyon da kuma gano hakikanin mutanen da abin ya shafa. Ta kuma ce akwai sabani kan adadin wadanda aka sace, lamarin da ya hana fitar da ainihin adadin a hukumance.
Duk da wannan bayani, masu sukar gwamnan sun ci gaba da nuna rashin jin dadinsu a shafukan sada zumunta, suna cewa ya kamata fifikon gwamna ya kasance kare rayuka da dukiyoyin al’ummarsa maimakon batun lashe zabe a wata jiha.
Rahotanni sun kuma nuna cewa wasu mazauna yankunan Ira, Inaja da Aho sun fara barin gidajensu sakamakon wasikun barazana da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka ajiye, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da kokarin shawo kan matsalar da maido da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.