Gwamnatin jihar Zamfara ta sake bude makarantu 45 daga cikin 75 da ta rufe saboda rashin tsaro

Gwamnatin jihar Zamfara ta sake bude makarantu 45 daga cikin 75 da ta rufe saboda rashin tsaro, kamar yadda ma’aikatar ilimi ta sanar yau Laraba a Gusau babban birnin jihar.

Babban Sakataren a ma’aikatar, Alhaji Kabiru Attahiru ne ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin ‘yan kungiyar fasaha ta jihar kan harkokin ilimi a cikin gaggawa wadanda suka kai ziyarar neman shawara a ma’aikatar.

Kafin hakan dai Gwamnatin jihar ta bayar da umarnin rufe makarantun ne a watan Satumbar 2021 bayan sace daliban makarantar Sakandaren gwamnati da ke garin Kaya a karamar hukumar Maradun ta jihar.

Alhaji Kabiru Attahiru ya ce dukkan makarantun 75 sun fada cikin yanayin rashin tabbas a lokacin da aka rufe su.

Babban Sakataren ya yabawa kungiyar da ake kira da Education in Emergency a wannan ziyara tare da ba su tabbacin ma’aikatar ta kudiri aniyar ci gaba da hada hannu da duk masu ruwa da tsaki domin bunkasa harkar ilimi a jihar.

Comments (0)
Add Comment