Ministan ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa gwamnati za ta gyara ginin gadar Third Mainland da ke Legas a kan Naira tiriliyan 3.6.
Ya ce barin gadar a mummunan yanayin da take ciki yanzu zai zama babban kuskure, domin gadar ce tafi kowacce samun zirga-zirga a kasar.
Ministan ayyukan ya bayyana hakan ne ga manema labarai a ranar Laraba bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) a Abuja, inji rahoton Tribune.