Gwamnonin Jihohi 16 sun nuna goyon bayansu na samarda ‘yan sandan jihohi

Gwamnonin Jihohi 16 sun mika rahoton nuna goyon bayansu na samarda ‘yan sandan jihohi ga majalisar tattalin arzikin kasa.

Sun kuma ba da shawarar yin sauye-sauye a kundin tsarin mulkin kasar nan don ba da damar kafa ‘yan sandan jihohi.

Rahotannin na daga cikin shawarwarin da aka bayar samu a taron majalisar zartarwa karo na 140 wanda mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya jagoranta a fadar gwamnati dake Abuja ranar Alhamis.

A cewar sanarwar, majalisar zartaswa ta kasa tana jiran rahotanni daga jihohi 20. Al’ummar kasar nan dai na fama da tashe-tashen hankula na sace-sacen jama’a, da hare-haren ‘yan bindiga lamarin da ya sake farfado da kiraye-kirayen kafa tsarin ‘yan sanda da dama ciki har da ‘yan sandan jihohi.

Comments (0)
Add Comment