Hukumar Lafiya ta Duniya ta bukaci gwamnatocin jihohin Najeriya su kara kudin allurar rigakafi

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bukaci gwamnatocin jihohin Najeriya su kara kudin da suke sanya wa a bangaren rigakafi domin karfafa samun allurar rigakafi a tsakanin al’umma, musamman bayan koma baya da aka samu sakamakon annobar COVID-19.

Daraktan WHO na rikon kwarya a Afrika, Dr Chikwe Ihekweazu, ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da makon rigakafi a Afrika da aka gudanar a jihar Ribas, yana mai jaddada cewa rigakafi hakki ne kuma jari ne ga lafiyar al’umma.

Ya bayyana cewa sama da yara miliyan shida a nahiyar Afrika ba su samu kowanne irin rigakafi ba a shekarar 2023, lamarin da ke barazana ga lafiyar al’umma tare da bazuwar cututtuka kamar sankarau da polio.

WHO ta bukaci a kara himma wajen cimma manufofin Shirin Rigakafi na 2030, tare da bukatar hadin kai daga gwamnati, da al’umma da kungiyoyin kasa da kasa don tabbatar da rigakafi ga kowa.

Comments (0)
Add Comment