Hukumar Shari’ar Musulunci ta Jihar Kano ta aurar da wasu mata da suka musulunta, inda ta dauki nauyin aurensu; da saya musu gadajensu da sauran kayan daki da kayan kicin.
Daraktan gudanarwa na hukumar, Auwal Lamido, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa yau a Kano cewa hukumar ta kuma warware wasu kararraki bakwai da suka shafi rikicin shugabanci a masallatai da makarantun Islamiyya cikin watanni biyu.
A cewar daraktan, an warware matsalolin a watan Maris da Afrilu na wannan shekara.
Auwal Lamido ya bukaci jama’a da su tabbatar suna yin dabi’u masu kyau da tsoron Allah SWT a cikin mu’amalarsu.
An kafa hukumar ne a shekara ta 2001 a matsayin ofishin kula da harkokin zamantakewa na musulunci, amma an daga darajarta zuwa Hukumar Shari’a a ranar 7 ga Nuwamban 2003.
Aikinta shi ne dabbakawa, tursasawa da kuma inganta dabi’un addinin musulunci da na al’adu a jihar.