Jam’iyyar PRP ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta shawo kan matsalar tattalin arziki

Jam’iyyar People’s Redemption Party, PRP, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta shawo kan matsalar tattalin arziki da tabarbarewar matsalolin tsaro a kasar nan.

Mukaddashin Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar PRP, Mista Muhammed Ishaq, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abuja.

Abin takaici ne ganin yadda jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta jagoranci gwamnati ta yi amfani da zarge-zargen da ba su da tushe balle makama da fargaba a yunkurin kawar da hankalinsu daga halalcin damuwar da al’ummar Najeriya ke nunawa.

A cewarsa, maimakon a ce masu zanga-zangar a matsayin ‘yan amshin shatan ‘yan adawa, kamata ya yi gwamnati ta saurari korafe-korafensu, ta kuma yi kokarin ganin ta magance matsalar rashin jin dadi. Ishaq ya ce ta hanyar tattaunawa da hadin kai na gaske ne za a iya samar da mafita mai ɗorewa ga ƙalubalen ƙasar.

Comments (0)
Add Comment