Kwamishiniyar Jin-kadai da Inganta Rayuwar Al’umma ta Jihar, Hajiya Hafsat Baba ta sanar da haka a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN a birnin Kaduna, yayin da ta ce, jihar ta kuma karbi sama da Almajirai dubu 1 daga wasu jihohin daban.
Kwamishiniyar ta ce, wannan matakin da aka dauka, na cikin yunkurin gwamnatin jihar na tabbatar da cewa, dukkanin kananan yara sun samu ilimin Al-Kur’ani da na zamani karkashin kulawar iyayensu.
Hajiya Hafsat ta ce, Ma’aikatarta tare da agajin Asusun Tallafa wa Ilimin Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNIECF, na kula da Almajiran da wasu jihohin suka taso keyarsu zuwa Kaduna.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Gidan radiyon RFI ya rawaito cewa, Kwamishiniyar ta ce, wasu daga cikin Almajiran na fama da wasu nau’ukan cutuka da ke bukatar kulawa kafin sake sada su da dangoginsu.
Bullar abbobar coronavirus ce ta tilasta wa gwamnatocin johohin arewacin Najeriya mayar da dubban Almajirai jihohinsu na asali.