Kungiyar ECOWAS ta ce ta sanya batun tsaro a gaba yayin da take kokarin cimma bunkasar tattalin arziki ta kashi biyar cikin dari a yankin Afirka ta Yamma, bisa la’akari da yadda matsalolin tsaro ke ci gaba da shafar wasu kasashe.
An bayyana cewa kungiyar ta karfafa tsarin tsaronta, ciki har da rundunar ECOWAS Standby Force da rundunar yaki da ta’addanci mai mambobi 1,650, duk da kalubalen da ke tattare da rage hadin kai da kasashen Sahel da suka fice daga kungiyar.
Duk da wadannan matsaloli, rahotanni sun nuna cewa tattalin arzikin yankin yana da karfi, inda aka samu bunkasar kashi 4.6 cikin dari a 2025 tare da hasashen kaiwa kashi biyar a 2026 sakamakon gyare-gyaren tsari da karin zuba jari.
ECOWAS ta kuma jaddada kin amincewarta da juyin mulki, ta bukaci sauyin siyasa mai gajeren zango a Guinea-Bissau, tare da cewa burin samar da Afirka ta Yamma mai zaman lafiya da hadin kai na nan daram duk da kalubalen siyasa da tsaro da yankin ke fuskanta.