Kimanin sa’o’i kaɗan bayan Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), jagoran jam’iyyar na ƙasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya gudanar da wata ganawa da ƙungiyoyin Kwankwasiyya daban-daban a gidansa da ke Miller Road, Kano.
Ƙungiyoyin, waɗanda suka fito daga sassa daban-daban na jihar, sun ziyarci Kwankwaso ne domin sake jaddada biyayyarsu tare da alkawarin ci gaba da goyon bayan akidarsa ta siyasa.
Da yake jawabi ga taron, Kwankwaso ya yi kira ga matasa da mambobin tafiyar Kwankwasiyya da su ci gaba da tsayawa tsayin daka kan ƙa’ida da akida, yana mai gargaɗin su da kada kuɗi ko wasu tayin siyasa su rinjaye su.
“Kasancewarmu a nan a yau ta ta’allaka ne bisa akida,” in ji shi. “Da mun bari kwaɗayi ya jagorance mu, da an saye mu da kuɗi tun tuni.”
Ko da yake Kwankwaso bai ambaci Gwamna Yusuf kai tsaye ba, kuma bai yi nuni da sauya shekar gwamnan daga jam’iyyar NNPP ba, masu sharhi kan siyasa na ganin kalaman nasa a matsayin martani a kaikaice ga matakin da gwamnan ya ɗauka na ficewa daga jam’iyyar.
Tun da farko a ranar Juma’a, Gwamna Yusuf ya sanar da murabus dinsa daga NNPP a hukumance, yana mai danganta hakan da abin da ya bayyana a matsayin rikice-rikicen cikin gida da ke ci gaba da addabar jam’iyyar. Wannan bayani na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu.
A cewar sanarwar, gwamnan ya miƙa wasiƙar murabus dinsa ga shugaban jam’iyyar NNPP na mazabarsa da ke Diso, a Karamar Hukumar Gwale ta Jihar Kano.
Waɗannan abubuwa guda biyu sun ƙara rura wutar sauye-sauyen siyasa a Kano, inda masu nazari ke sanya ido sosai kan tasirin da hakan zai yi ga yanayin siyasar jihar, musamman gabanin fafatawar siyasa na gaba.