Akalla mutane 19 ne aka tabbatar da mutuwarsu a karamar hukumar Doguwa da ke jihar Kano bayan da ambaliyar ruwa tayi awon gaba da wata mota da suke tafiya a ciki.
An rawaito cewa lamarin ya faru ne a daren Juma’a bayan wani ruwan sama da aka yi kamar da bakin kwarya a yankin.
HakiminDoguwa, Alhaji Yusif Umar Doguwa, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce ya zuwa yanzu, an gano gawawwaki 15 yayin da aka tsananta bincike don gano sauran mutane 4 da iftila’in ya rutsa da su.
Umar Doguwa ya ce ambaliyar ruwan ta yi awon gaba da motar ne bayan injin ta ya mutu a tsakiyar wata gada da suke kokarin tsallakawa.
Ya bayyana cewa ambaliyar ruwan ta mamaye gadar sakamakon ruwan sama da aka tafka a daren Juma’a.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar, Ali Abdullahi Garko shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.