Mutum 25 Sun Mutu A Hare-Haren ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Gabashin Najeriya

Aƙalla mutum 25 ne suka rasa rayukansu a wasu hare-haren da ake zargin mayaƙan ƙungiyar Boko Haram ne suka kai a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya, kamar yadda wasu majiyoyi na cikin gida suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

Majiyoyin sun ce hare-haren sun faru ne a garuruwan Madagali da Hong, yankunan da ke kan iyaka da ƙasar Kamaru, inda mayaƙan Boko Haram suka daɗe suna kai hare-hare tun bayan fara tayar da ƙayar baya a shekarar 2009.

Wani jami’in ƙaramar hukumar Madagali ya ce maharan sun kai farmaki kasuwa da yammacin Talata inda suka buɗe wuta kan jama’a.

“Sun zo ne a kan babura da dama, suka fara harbi tare da kashe mutum 21,” in ji jami’in, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa. Ya ƙara da cewa ana ci gaba da laluben gawarwaki, domin wasu na iya mutuwa a daji yayin da suke ƙoƙarin tserewa.

Majiyar ta ce maharan sun kuma kwashe kayayyakin abinci tare da sace babura a kasuwar.

A garin Hong ma, an kashe wasu mutum huɗu ciki har da sojoji uku, kamar yadda wani mazaunin yankin ya shaida wa AFP. Ya ce an gano gawarwakin sojojin uku da wata mata guda bayan harin.

Rahotanni sun ce duk da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankin, wasu daga cikin mazauna garin sun fara barin gidajensu saboda fargaba.

Gwamnan jihar Adamawa, Adamu Umaru Fintiri, ya yi Allah wadai da hare-haren, yana mai cewa gwamnati ba za ta bari ‘yan ta’adda su kawo cikas ga ƙoƙarin dawo da zaman lafiya ba.

Tun daga shekarar 2009, rikicin ya samo asali ne daga tayar da ƙayar baya ta Boko Haram da kuma ɓangaren ta na Islamic State West Africa Province ya yi sanadin mutuwar fiye da mutum 40,000 tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu a arewa maso gabashin Najeriya, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.

Rikicin ya kuma bazu zuwa ƙasashen Nijar, Chadi da Kamaru, lamarin da ya sa aka kafa rundunar haɗin gwiwa ta ƙasashen yankin domin yaƙi da ƙungiyoyin.

Sai dai rundunar ta fuskanci ƙalubale a ‘yan shekarun nan, musamman bayan janyewar Nijar sakamakon saɓanin diflomasiyya da Najeriya bayan juyin mulkin soji na 2023.

A farkon watan nan ma, rundunar sojin Amurka ta sanar da fara tura sojoji kusan 200 zuwa Najeriya domin bayar da horo da tallafin fasaha ga dakarun ƙasar wajen yaƙi da ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.

Comments (0)
Add Comment