NIS Ta Gargadi ’Yan Najeriya Kan Yaduwar Shafukan Daukar Ma’aikata Na Bogi

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya, wato Nigeria Immigration Service (NIS), ta gargadi jama’a kan yawaitar wasu shafukan yanar gizo na bogi da ke ikirarin daukar ma’aikata a madadin hukumar.

Hukumar ta yi wannan bayani ne a wani sakon da ta wallafa a shafinta na X a ranar Talata, inda ta bayyana cewa babu wani daukar ma’aikata da take yi kai tsaye a halin yanzu.

A cewar NIS, daukar ma’aikata guda daya tilo da ke gudana a hukumomin tsaro shi ne wanda Hukumar CDCFIB ke gudanarwa, wato Civil Defence, Correctional, Fire and Immigration Services Board.

Hukumar ta bukaci duk masu neman aiki da sauran jama’a da su rika dogaro ne kawai da shafin yanar gizon CDCFIB na hukuma domin samun sahihin bayani da sabbin bayanai kan daukar ma’aikata.

NIS ta jaddada cewa duk wasu shafuka, hanyoyin sadarwa ko tallace-tallacen daukar aiki da ke yawo ba su da izini, kuma ya kamata jama’a su yi watsi da su gaba daya.

Hukumar ta kuma gargadi masu neman aiki da su yi taka-tsantsan kada su fada hannun ‘yan damfara da ka iya amfani da shafukan bogi wajen karbar kudade ko tattara bayanan sirri da sunan daukar ma’aikata.

A karshe, NIS ta bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani shafin yanar gizo ko tallan daukar aiki da suke zargi ga hukumomin da suka dace, domin kare al’umma da tabbatar da gaskiya a harkar daukar ma’aikata.

Comments (0)
Add Comment