Sojoji Sun Ce Sun Ceto Mutum Biyar da Aka Sace A Kogi

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun samu nasarar ceto mutum biyar da aka sace a jihar Kogi, yayin da waɗanda suke yi garkuwa da su suka tsere sakamakon hare-haren soji da ake ci gaba da kai musu.

An samu wannan nasara ne a ranar 17 ga watan Yuni 2026, yayin da sojojin ke ƙara zafafa kai hare-hare kan maɓoyar ‘yan ta’adda a cikin dazukan jihar.

A wani samamen toshe hanyoyi da aka gudanar daga sansanin sojin Oshokoshoko zuwa hanyar Adankolo ne sojojin suka gano mutanen da aka sace bayan da maharan suka yi watsi da su suna tserewa.

Rahotanni na farko sun nuna cewa mutanen sun samu ‘yancinsu ne bayan da sojojin suka tilasta maharan tarwatsewa sakamakon hare-haren sama da ƙasa da aka kai musu.

Daga nan ne aka kwashe su zuwa wurin da ke da tsaro, sannan aka kai su cibiyar lafiya ta soji domin ci gaba da kula da su.

Rundunar sojin ta ce ana ci gaba da tattara bayanan sirri daga hannun wadanda aka ceto domin taimakawa wajen gano sauran ‘yan ta’addar da ke aiki a yankin, tare da tabbatar da cewa za a ci gaba da matsa musu lamba har sai an murƙushe dukkan sansaninsu.

Comments (0)
Add Comment