Sojoji sun kashe mayaka sama da 120 na Boko Haram da ISWAP a yankin Arewa maso Gabas

Helkwatar tsaro tace dakarun operation Hadin Kai sun kashe mayaka sama da 120 na Boko Haram da ISWAP a yankin Arewa maso Gabas cikin makonni uku da suka gabata.

Daraktan Yada Labarai na Helkwatar Tsaro, Bernard Onyeaku, ya sanar da haka yayinda yake bayyana cigaban da aka samu a ayyukan sojoji a fadin kasarnan tsakanin ranar 20 ga watan Janairu zuwa watan Fabrairu da muke ciki a Abuja.

Onyeaku yace a lokacin luguden wuta ta sama da ta kasa, an kashe kwamandojin ISWAP da Amir din su cikin har da mayakan kasashen waje wadanda suke hada bama-bamai.

Ya kuma ce mayaka 965 da iyalansu sun mika wuya ga sojoji a gurare daban-daban cikin makonnin.

Onyeaku yace mutane 104 daga cikin mayakan da suka mika wuya, ‘yan kungiyar ISWAP ne, yayin da aka ceto mutane 25 da aka sace.

Comments (0)
Add Comment