Sojojin Isra’ila Sun Kashe Falasɗinawa 12 A Sassa Daban-Daban Na Gaza

Aƙalla Falasɗinawa 12, rabinsu yara, sun mutu a Zirin Gaza tun daga wayewar gari, yayin da aka ruwaito hare-hare a Rafah, kwana guda kafin a sake buɗe mashigar Rafah da ke haɗa Gaza da Masar.

Wani harin sama da Isra’ila ta kai a al-Mawasi ya kashe mutum bakwai, ciki har da yara uku, yayin da wani harin a unguwar Remal ya kashe biyar. Haka kuma mutane takwas sun jikkata a unguwar Daraj.

Tun daga fara tsagaita wuta a 10 ga Oktoba aƙalla Falasɗinawa 524 sun mutu sakamakon hare-haren Isra’ila, wanda yaƙin kisan kare dangi ke ci gaba da kashe fiye da 71,600 tun 7 ga Oktoba, 2023.

Mashigar Rafah za ta buɗe ne kawai ga “takaitaccen zirga-zirgar mutane” waɗanda suka samu amincewar tsaro, ba tare da shigowar kayan agaji ba. Hamas ta bukaci Isra’ila ta ba da damar shiga da fita ba tare da ƙuntatawa ba.

Comments (0)
Add Comment