Wasu yan bindiga sun sace matar wani mutum mai suna Aliyu Mai-Yadi Charanchi tare da dansa dan shekara uku, a yankin karamar hukumar Charanci dake jihar Katsina.
Mazauna garin sun ce lamarin ya auku da misalin karfe 12 da rabi na ranar Talata.
An rawaito cewa yan bindigar sun tunkari gidan mutumin dake Unguwar Gabas a Charanchi.
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
- Karyewar gada ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 24 a lardin Guangdong na kudancin kasar China
- Isra’ila na dab da fara kai hare-hare birnin Rafah na kudancin Gaza ta ƙasa – Martin Griffiths
- Gwamnonin jahohin arewa sun bayyana damuwa bisa cigaba da karuwar rashin tsaro a shiyyar
- Gwamnatin Tarayya ta shirya tsaf domin bayar da cikakkiyar dama ga matatar man fetur ta Dangote
Ba za a iya tabbatar da ko yan bindigar mahara ne ko wasu bata gari ne dake garkuwa da mutane domin samun kudin fansa ba.
Kakakin rundunar yansandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya kara da cewa har yanzu ana sauraron cikakken bayanin abinda ya faru daga baturen yan sanda na yankin.