Wasu yan bindiga sun sace matar wani mutum mai suna Aliyu Mai-Yadi Charanchi tare da dansa dan shekara uku, a yankin karamar hukumar Charanci dake jihar Katsina.
Mazauna garin sun ce lamarin ya auku da misalin karfe 12 da rabi na ranar Talata.
An rawaito cewa yan bindigar sun tunkari gidan mutumin dake Unguwar Gabas a Charanchi.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Ba za a iya tabbatar da ko yan bindigar mahara ne ko wasu bata gari ne dake garkuwa da mutane domin samun kudin fansa ba.
Kakakin rundunar yansandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya kara da cewa har yanzu ana sauraron cikakken bayanin abinda ya faru daga baturen yan sanda na yankin.