Daga cikin kwamandojin da suka mika wuya akwai Abu Radda, Maikada, Umar Black da Tukur Dan Najeriya, wadanda kowannensu ke da daruruwan matasa karkashinsu.
Kwamared Hamisu Sai’idu Batsari ya bayyana cewa:
“Kowannensu musamman Abu Radda na da yaran da suka kai 500 karkashinsa. Su Tukur Mairakumi da Maikada da Dan Najeriya suna da daruruwan mabiyansu,”
Ya kara da cewa wasu daga cikin wadannan kwamandojin na rike da makamai ne domin kare kansu daga sauran barayin daji da ba su yarda da sulhu ba.