Hukumar samar da ayyukan yi ta kasa ta fara bayar da horo ga matasa dubu 1 da 350 a jihar Jigawa.
Jagoran hukumar na jiharnan, Malam Abubakar Jamo, ya sanar da haka a wata ganawa da kamfanin dillancin labarai na kasa a Dutse.
Abubakar Jamo yace aikin horon na watanni 3 wanda aka fara a wannan watan na Oktoba, za a gudanar da shi a karkashin shirin hukumar na koyar da sana’o’in hannu.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Yayi bayanin cewa an zabo mutane 50-50 daga kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomin jiharnan 27 domin cin gajiyar shirin.
Abubakar Jamo ya kara cewa za a bayar da horo akan gyaran mota da dinki da gyaran injinan wuta da aikin komfuta da kafinta da gyaran wayar hannu da aikin jima da aski da kuma zane-zane.
Jagoran yayi nuni da cewa za a bayar da horon ne da nufin rage zaman kashe wando tsakankanin matasa a jiharnan.