Ɗan Takara Ɗaya Ba Zai Zama Tilas Ga ‘Yan Najeriya Ba – Rabiu Musa Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi gargadi ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) cewa ba za su iya tilasta ɗan takara ɗaya ga ‘yan Najeriya a zaben 2027 ba.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a asusun sa na X mai tabbaci.

Ya shawarci INEC da su bai wa ‘yan ƙasa damar zaɓar shugabanninsu cikin ‘yanci, ba tare da la’akari da jam’iyyar da suka fito ba.

A cewar sa:
“Yau na haɗu da shugabannin African Democratic Congress (ADC) da sauran masu rajin dimokuradiyya a wani taron manema labarai na duniya domin sukar nuna bambancin ra’ayi da rashin adalci daga INEC.”

“Na goyi bayan matsayar taron: A 2027, dole ne a bai wa ‘yan Najeriya damar zaɓar shugabanninsu daga jam’iyyun siyasa daban-daban. Hukumar zaɓe ba ta da ikon tilasta ɗan takara ɗaya a mafi girman da kuma dimokuradiyyar Najeriya.”

Comments (0)
Add Comment