Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya shigar da yara dubu 3, yawancinsu yayan talakawa, a manyan makarantu na musamman guda 2 dake kananan hukumomin Maiduguri da Jere.
Gwamnatinsa ce ta gina makarantun a yankunan kananan hukumomin Maiduguri da Jere dake da yaran dayawa da basa zuwa makaranta. An shirya makarantun da nufin kula da karatunsu.
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
- Karyewar gada ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 24 a lardin Guangdong na kudancin kasar China
- Isra’ila na dab da fara kai hare-hare birnin Rafah na kudancin Gaza ta ƙasa – Martin Griffiths
- Gwamnonin jahohin arewa sun bayyana damuwa bisa cigaba da karuwar rashin tsaro a shiyyar
- Gwamnatin Tarayya ta shirya tsaf domin bayar da cikakkiyar dama ga matatar man fetur ta Dangote
Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mallam Isa Gusau, ya fitar, tace gwamna Zulum ya sanar a ranar Litinin yayin bude makarantun cewa gwamnati zata mika su ga al’umma domin su gudanar da su, yayin da gwamnatin zata biya albashin malamai.
A wani cigaban kuma, gwamnan ya kaddamar da sabon titin da magudanan ruwa a unguwar Maromaro dake Maiduguri.