Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya shigar da yara dubu 3, yawancinsu yayan talakawa, a manyan makarantu na musamman guda 2 dake kananan hukumomin Maiduguri da Jere.
Gwamnatinsa ce ta gina makarantun a yankunan kananan hukumomin Maiduguri da Jere dake da yaran dayawa da basa zuwa makaranta. An shirya makarantun da nufin kula da karatunsu.
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
- EFCC sun kai samame gidan tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello da ke Abuja
- Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP a Najeriya ya bayyana goyon bayansa ga Umar Damagum
- MƊD za ta ƙaddamar da asusun neman taimako domin samar da kayan agaji ga Falasɗinawa a Gaza
- Gwamnan Jihar Jigawa ya nemi ma’aikatun jihar da su cimma yarjejjeniyar da jihar ta kulla da Ofishin FCDO
Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mallam Isa Gusau, ya fitar, tace gwamna Zulum ya sanar a ranar Litinin yayin bude makarantun cewa gwamnati zata mika su ga al’umma domin su gudanar da su, yayin da gwamnatin zata biya albashin malamai.
A wani cigaban kuma, gwamnan ya kaddamar da sabon titin da magudanan ruwa a unguwar Maromaro dake Maiduguri.