Asusun kiwon lafiya na jihar Jigawa yace kawo yanzu asibitoci masu zaman kansu guda 10 ne suka nuna sha’awarsu ta shiga shirin asusun adashen gata na kiwon lafiya na jiha.
Sakataren zartarwa na asusun Dr Nura Ibrahim ya sanar da haka ga Radio Jigawa.
Yace daga cikin asibitocin masu zaman kansu da suka yi rijistar shiga shirin sun hadar da guda uku a garin Hadejia da daya a Dutse da daya a Ringim da uku a Kazaure da kuma daya a Maigatari da daya a Babura.
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
- Gwamnati na shirin farfado da masaku da nufin bunkasa noman auduga da samar da tufafi
- Hukumomi na aiki da jami’an tsaro wajen kamo duka ragowar fursunoni 109 da suka tsere daga gidan gyaran hali
- Za’a gudanar da cikakken bincike don tabbatar da ingancin duka jiragen sama da ke zirga-zirga a Najeriya
Dr. Nura Ibrahim yace kawo yanzu sun shigar da ma’aikatan jiha da kananan hukumomi da na sashen ilmi dubu 25 da 116 ne aka yiwa rijista kawo yanzu.
Yace a mako mai zuwa jirgin rijistar zai ziyarci kananan hukumomin Mallam Madori da Auyo da Kaugama.