Shugaban Sojojin Kasa, Laftanal Janar Tukur Burutai yayi gargadin cewa sojoji baza su kyale bata gari su tarwatsa zaman lafiyar Najeriya ba.
Mukaddashin daraktan hulda da jama’a na hukumar soji, Kanal Sagir Musa, yace Buratai ya fadi hakan a jiya yayin zaman ganawa da manyan jami’an soji da kwamandojin barikoki da na filin yaki, wanda aka gudanar a Abuja.
Sagir Musa ya yiwa yan jarida jawabi akan abin da aka tattauna a zaman ganawar, lokacin da yake zantawa da manema labarai.
Tukur Buratai ya gayawa manyan jami’an soji da kwamandojin barikoki da na filin yaki cewa babu hurumin rashin biyayya tsakankanin dukkan jami’ai da sojojin Najeriya.
- An tsare wani mataimakin ministan tsaron kasar Rasha bisa zargin karbar cin hanci
- An dakatar da Daraktan kwalejin Birnin Kudu da jami’in kula da harkokin abinchi na kwalejin
- Gwamna Namadi yayi kira ga sabbin masu yiwa kasa hidima da aka turo jihar jigawa da su kasance jakadu na gari
- Majalisar dokokin jihar Jigawa ta kafa kwamatin wucin gadi domin nazari kan dokar hukumar zabe
- Jam’iyyar PDP za ta gudanar da babban taronta a jihohi 25 domin zaben sabbin shugabanni
Ya bayar da umarnin cewa dole su jaddadawa na kasa da su cewa hukumar soji ta jajirce wajen tabbatar da dorewar mulkin demokradiyya a Najeriya, kasancewar ita ce hanya daya tilo wajen samar da cigaba.