A wani labarin na jam’iyyar APC, an kashe mutum daya a jihar Jigawa a wani gangamin yakin neman zaben jam’iyyar a karamar hukumar Kazaure. Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Emmanuel Ekot, ya shaida wa manema labarai cewa, ‘yan sandan na bin sahun wanda ake zargi da kisan wanda aka ce ya gudu zuwa Continue reading
Bankin CBN ya musanta karancin sabbin takardun kudaden Naira kamar yadda wasu ‘yan Najeriya ke zargi
Babban bankin kasa, CBN, ya musanta karancin sabbin takardun kudaden Naira kamar yadda wasu ‘yan Najeriya ke zargi. Gwamnan babban bankin kasar, Godwin Emefiele, wanda ya samu wakilcin daraktan sashen kula da tsarin biyan kudi na bankin, Musa Jimoh, ya musanta zargin a wani taron manema labarai a Jos, babban birnin jihar Filato. Godwin Emefiele […]Continue reading
A yau ne ake sa ran shugaban kasa Muhammad Buhari zai kaddamar da masana’antar shinkafa ta Darma a Katsina, kamar yadda sanarwar da mahukuntan sabon kamfanin suka fitar a jiya. Kamfanin mallakin hamshakin dan kasuwa Alhaji Dahiru Barau Mangal ne. Kamfanin wanda a shirya kaddamarwar, yana injunan da ke sarrafa kansu tare da ingantattun injunan […]Continue reading
Mai martaba sarkin Kazaure, Alhaji Najib Hussain Adamu ya hori mata musulmi da su kara tashi tsaye wajen neman ilmin addini da na zamani domin sanin yadda zasu bautawa Allah SWT. Sarkin ya yi kiran ne a lokacin bikin saukar karatun dalibai 55 na makarantar Madarasatul Ummil Mu’umimina Aisha Islamiyya Kazaure. Sarkin wanda ya samu […]Continue reading
Hukumar Kididdiga ta Kasa, NBS, ta ce hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya ya ragu zuwa kaso 21.34 a ma’aunin shekara-shekara a watan Disamban 2022. Hakan yazo ne cikin rahoton kididdigar farashin masu sayen kayayyaki da kuma hauhawar farashin kayayyaki na watan Disambar 2022 da aka fitar jiya a Abuja. Rahoton ya ce adadin ya nuna […]Continue reading
Gwamnatin jihar Jigawa ta tura kudaden yarjejeniyar karatu na daliban makarantar koyar da fasahar sadarwa ta zamani dake Kazaure zuwa kasar Singapore. Shugaban makarantar, Farfesa Babawuro Usman ya sanar da hakan a lokacin da yake tilawar nasarorin da makarantar ta samu a shekarar 2022. Yace an biya kudaden makarantar ne ga daliban dake karatun kwasa […]Continue reading
Gwamnan babban bankin kasa CBN Godwin Emefiele ya koma bakin aiki bayan hutun da yake yi a kasar waje. Gidan Rediyon Sawaba ya bayar da labarin yadda jami’an tsaron SSS suka mamaye hedikwatar CBN tare da kwace ofishin Godwin Emefiele a jiya da yamma. Duk da cewa kakakin hukumar SSS, Peter Afunanya, ya musanta mamayar, […]Continue reading
Ya yin da ake nuna damuwa kan yadda cutar korona ke kara yaduwa a kasar China, da wasu sassan duniya, Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce har yanzu amfani da takunkumin rufe fuska ya na bada kariya daga kamuwa da korona tare da bukatar a ci gaba da amfani da shi. A sabbin alkalumman da […]Continue reading
Aisha Bichi, uwargidan babban daraktan hukumar tsaron farin kaya ta SSS, Yusuf Bichi, ta bayar da umarnin kama dan takarar gwamnan jihar Kano na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf, tare da hana shi shiga jirgin Air Peace daga Kano zuwa Abuja a daren Lahadi. An rawaito cewa rikicin ya fara ne a kofar wajen zaman […]Continue reading
Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur, Cif Timipre Sylva, a jiya, ya ce Kamfanin Mai na Kasa (NNPC) yana asara wajen sayar da man fetur saboda umarnin da gwamnatin tarayya ta ba shi bisa tallafin mai. Kalaman na Timipre Sylva na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan kasuwar mai suka bayyana cewa, matsalar samar da […]Continue reading