Jihar Jigawa, 21 ga Janairu, 2026 – A taron farko na Kwamitin Zartarwa na Jihar Jigawa a shekarar 2026, Gwamna Malam Umar A. Namadi, FCA, ya jagoranci taron inda aka yanke wasu muhimman shawarwari da suka shafi bunkasa tattalin arzikin jihar da horar da matasa.
Karfafa Jigawa State Savings and Loans Limited
Kwamitin ya amince da Naira Biliyan 1 (₦1,000,000,000) domin karfafa jarin Jigawa State Savings and Loans Limited. Wannan kudin zai taimaka wa bankin wajen cika ka’idojin Babban Bankin Najeriya (CBN) na Primary Mortgage Banks da tabbatar da dorewar bankin.
An bayyana cewa matakin zai tabbatar da kariya ga kudaden masu ajiya, bunkasa rancen gidaje, da habaka harkokin kudi a jihar. Haka kuma, Gwamnatin ta sake jaddada muhimmancin gudanar da aikin, gaskiya, da bin ka’idoji a dukkanin cibiyoyin gwamnati.
Shirin Hadin Gwiwa da Rasha a Harkar Noma 2026/2027
Bugu da ƙari, Kwamitin Zartarwa ya amince da Naira Miliyan 172.3 domin tallafa wa ɗan asalin jihar Jigawa don shiga Jigawa–Russia Agricultural Capacity Cooperation Programme. Shirin zai ba matasa damar samun horo na ilimi a matakin digiri na biyu da na uku (Master’s da PhD) a fannoni daban-daban na noma.
An ce horon zai taimaka wajen samar da sabbin dabaru, bincike mai zurfi, da ilimin zamani wanda zai bunkasa noma, tsaron abinci, da habaka tattalin arziki a jihar.
Gwamnatin Jigawa ta jaddada cewa horar da matasa da samun hadin gwiwa da kasashen waje su ne muhimman hanyoyi wajen inganta rayuwar al’umma, samar da aikin yi, da tabbatar da ci gaban tattalin arzikin jihar.