Akalla mutane 360 ne aka kashe fadin jihar Kaduna daga watan Janairu zuwa watan Maris na 2022 a rikicin kabilanci da kuma ta’addanci

Kwamishinan tsaro da cikin gida na jihar Kaduna Samuel Aruwan, yace akalla mutane 360 ne aka kashe fadin jihar daga watan Janairu zuwa watan Maris na 2022 a rikicin kabilanci da kuma ta’addanci.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a lokacin dayake kaddamar da rahoton tsaro na watanni ukun farkon wannan shekarar ga gwamnan jihar Nasir El-Rufai a birnin Kaduna.

Ya kara da cewa a watanni ukun farkon wannan shekarar anyi garkuwa da mutane 1,389 da santoriyar birnin Kaduna.

Inda yace ansace mutane 165 a Birnin Gwari, sai mutum 158 a Giwa, sai kuma karamar hukumar Igabi da mutane 263, sai kuma Chikun 287 da kuma karamar hukumar Kajuru 203.

A cewar Aruwan an sace kimanin mutane 249 ne a kudancin Kaduna a wasu  hare-haren ta’addanci a yankin.

Haka mutanen da aka kashe a birnin Kaduna yan ta’addane suka kashe su.

Ya kara da cewa a cikin watannin ukun farkon wannan shekarar anyi garkuwa da wasu mata dayawa, tare da yiwa 10 daga cikin su fyade.

Comments (0)
Add Comment